An haifi Sheikh Prof. Ibrahim Ahmad Maqari a ranar 15-09-1976 a birnin Zaria dake Jihar kaduna dake arewacin Najeriya.
farfesa Ibrahim Maqari Malamin Addinin Musulunci ne kuma mai bin darikar tijjaniya.
masanin karabci ne Wanda a Kansa ne yayi karatunsa har zuwa matakin farfesa.
yayi karatunsa na firamari a birnin katsina a shekaran 1987 a lokacin mahaifinsa yana aikin malanta a Katsina Arabic college, bayan dawowar mahaifin nasa gida Zaria, farfesa Ibrahim Maqari yayi karatun sakandire a Jama'atu Arabic school dake Zaria kafin daga bisani ya tafi kasar Masar inda yayi digirinsa na farko a jimi'ar Al'azhar dake birnin alkahiran masar a shekaran 1999.
bayan ya dawo gida najeriya ya cigaba da karatunsa a jimi'ar Ahmadu Bello Zaria inda anan ma yayi digirinsa na biyu duk a fannin larabci a shekaran 2005 kafin daga bisani ya tafi jami'ar Bayero dake Kano inda yayi digirin digirgir wato PhD a turance a fannin larabci a shekaran 2009 tare da koyarwa kafin daga bisani ya zama farfesa a jami'ar ta Bayero.
Ya Fara koyarwa a jami'ar Ahmadu Bello Zaria a shekaran 2009 kafin daga bisani ya koyar a jami'ar Jihar kaduna inda ya zama babban malami a shekaran 2010.
Farfesa Ibrahim Maqari ya koma jami'ar Bayero inda yayi karatun farfesa a fannin larabci da harsuna, ya kuma aje aikin koyarwa da Kansa a shekaran 2020.
Farfesa Ibrahim Maqari yayi karatun Addinin mai zurfi tun daga wajen mahaifansa da wasu manya-manyan Malamai a birnin Zaria kamar Malam tanimu kusfa da Malam Bala Kusfa. haka zalika farfesa Ibrahim Maqari ya haddace Alkur'ani mai girma tun yana dan shekara 14 a duniya a makarantar sheikh Yahuza zaria, ya kuma haddace manya-manyan Littafan hadisan Bukhari da Muslim.
Shine babban limamin masallacin juma'an kasa dake babban birnin tarayya Abuja inda yake gudanar da karatun Tafsir a lokacin watan Ramadan da sauran karatun fiqh.
Farfesa Ibrahim Maqari Yayi aure kuma Yana da 'Ya'ya inda ya aurar da daya daga cikinsu a shekaran 2024.
Article Translation in English Language.
Sheikh Prof. Ibrahim Ahmad Maqari on 15-09-1976 in Zaria city in Kaduna state in northern Nigeria. Professor Ibrahim Maqari is an Islamic teacher and a follower of the Tijjaniya sect. He is a classical scholar who has studied up to the level of a professor.
He did his primary education in Katsina city in 1987 when his father was working as a scholar at Katsina Arabic college, after his father returned home to Zaria, Professor Ibrahim Maqari studied high school at Jama'atu Arabic school in Zaria before he went to Egypt where He obtained his first degree at Al'azhar University in the capital city of Egypt in 1999.
After he returned home to Nigeria, he continued his studies at Ahmadu Bello University, Zaria, where he completed his second degree in Arabic in 2005 before he went to Bayero University in Kano where he completed his PhD in English.
In Arabic in 2009 and taught before becoming a professor at the University of Bayero. He started teaching at Ahmadu Bello University Zaria in 2009 before he later taught at Kaduna State University where he became a senior lecturer in 2010.
Professor Ibrahim Maqari moved to Bayero University where he studied as a professor in the field of Arabic and languages, and went to work teaching with Kansa in 2020.
Professor Ibrahim Maqari studied religion in depth from his parents with some great scholars in the city of Zaria such as Malam Tanimu Kusfa and Malam Bala Kusfa.
In the same way, Professor Ibrahim Maqari memorized the Holy Qur'an when he was 14 years old in the school of Sheikh Yahuza Zaria, and he also memorized the great books of hadiths of Bukhari and Muslim.
He is the chief imam of the National Mosque in the capital city of Nigeria, Abuja, where he conducts Tafsirul Qur'an during the month of Ramadan and other fiqh readings. Professor Ibrahim Maqari is married and has children where one of them got married in the year 2024.
0 comments: